DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta nemi a kara yi wa jami’an tsaron Nijeriya uzuri

-

Jam’iyyar APC ta yi kira da a kara hakuri da kuma bai wa jami’an tsaro goyon baya yayin da suke kokarin ceto yaran da aka sace da kuma yaki da matsalar tsaro a fadin Nijeriya.

A wata hira da Channels TV, kakakin jam’iyyar, Felix Morka, ya ce kare rayuwar yaran da aka sace shi ne babban abin da gwamnati ke muradi, don haka dole jami’an tsaro su yi aiki cikin taka tsantsan.

Google search engine

Ya ce ayyukan ceto yara na bukatar kulawa ta musamman saboda kuskure kadan na iya jefa su cikin hatsari. Morka ya roki ‘yan Najeriya da su nuna hakuri da fahimta ga kokarin rundunonin tsaro.

Rahoton jaridar Punch ya ce Morka ya kuma yaba da jajircewar sojoji da sauran jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu don kare kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara