Babu dokar da muka karya a saukar gaggawa da jirginmu ya yi a Burkina Faso in ji Rundunar sojin sama ta Nijeriya
Hukumomin sojin Nijeriya sun ce saukar gaggawa da jirginsu ya yi a birnin Bobo-Dioulasso na Burkina Faso matakin kariya ne da ya dace da ka’ida, ba kuma take dokar sararin samaniya ba.
A cikin wata sanarwa, Daraktan Yada Labarai na NAF, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce tawagar jirgin ta lura da wata matsala ta na’ura bayan tashinsu daga Legas zuwa kasar Portugal, abin da ya sa suka nufi filin jirgin da ya fi kusa domin saukar kariya, kamar yadda dokokin tsaro na kasa da kasa suka tanada.


