DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawa ta gayyaci ministan sufurin jiragen sama kan tsadar tikitin jirgi

-

Majalisar Dattawa ta gayyaci Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, da manyan masu ruwa da tsaki a bangaren sufurin jirage domin tattaunawar gaggawa bayan korafe-korafen jama’a game da tsadar tikitin jirgin sama a kasar.

Wannan matakin ya biyo bayan korafin da Sanata Buhari Abdulfatai ya gabatar, inda ya gargadi cewa hauhawar farashin jirgi na iya haifar da matsalar sufuri a fadin kasar, musamman yayin da ake shiga hutun karshen shekara.

Google search engine

A yayin tattaunawar, Sanata Buhari ya ce ‘yan Najeriya na kuka da tsadar jirgin cikin gida da ke kara tashi daga wata zuwa wata.

Ya bayyana cewa tikitin jirgi daga Abuja zuwa Legas yanzu ya kai tsakanin N400,000 zuwa N600,000, wanda ya sanya mutane da dama daina tafiya-tafiye ta sama.

Sanatan daga Jihar Oyo ya kara da cewa abin na kara dagule wa jama’a saboda matsalolin tsaro da wahalar tafiya a manyan hanyoyin mota.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Mafi Shahara