DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro

-

Najeriya da Masarautar Saudiyya sun kulla sabuwar yarjejeniya ta shekaru biyar domin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da dangantakar soja tsakanin kasashen biyu.

A cewar wata sanarwa daga Ofishin Sakataran Yaɗa Labarai na Ministan Tsaron kasar, Ahmed Dan Wudil, yarjejeniyar za ta haɗa da musayar bayanan leken asiri, horaswar soja, ƙera kayan tsaro, da haɗin gwiwa a fagen ayyukan tsaro domin bunƙasa zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Google search engine

Karamin Ministan Tsaron Nijeriya, Mohammed Matawalle, ya sanya hannu a madadin Najeriya, yayin da Dr Khaleed H. Al-Biyari ya wakilci Saudiyya.

Sanarwar ta ce wannan mataki babban ci gaba ne wajen ƙarfafa hulɗa, inganta haɗin kai da kuma yaki da sabbin kalubalen tsaro dake tasowa a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara