DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro

-

Najeriya da Masarautar Saudiyya sun kulla sabuwar yarjejeniya ta shekaru biyar domin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da dangantakar soja tsakanin kasashen biyu.

A cewar wata sanarwa daga Ofishin Sakataran Yaɗa Labarai na Ministan Tsaron kasar, Ahmed Dan Wudil, yarjejeniyar za ta haɗa da musayar bayanan leken asiri, horaswar soja, ƙera kayan tsaro, da haɗin gwiwa a fagen ayyukan tsaro domin bunƙasa zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Google search engine

Karamin Ministan Tsaron Nijeriya, Mohammed Matawalle, ya sanya hannu a madadin Najeriya, yayin da Dr Khaleed H. Al-Biyari ya wakilci Saudiyya.

Sanarwar ta ce wannan mataki babban ci gaba ne wajen ƙarfafa hulɗa, inganta haɗin kai da kuma yaki da sabbin kalubalen tsaro dake tasowa a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Zulum zai ba duk dan Borno da ke hijira a Kamaru N500,000

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa gwamnatin jiharsa za ta ba kowane ɗan gudun hijira ɗan Borno da yake a Kamaru...

Majalisar dattawa ta gayyaci ministan sufurin jiragen sama kan tsadar tikitin jirgi

Majalisar Dattawa ta gayyaci Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, da manyan masu ruwa da tsaki a bangaren sufurin jirage domin tattaunawar gaggawa bayan korafe-korafen...

Mafi Shahara