Jam’iyyar Accord ta ayyana gwamnan Osun Ademola Adeleke a matsayin dan takara daya tilo a zaben fidda gwanin gwamnan jihar
Kasa da sa’o’i 16 bayan Ademola Adeleke ya koma jam’iyyar Accord, shugabancin jam’iyyar na kasa ya amince da shi ya shiga zaben fidda gwani na gwamnoni.
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa Adeleke ya sauya sheka ne da yammacin Talata tare da mataimakinsa, Kola Adewusi, da wasu manyan jami’ai.
Shugaban kwamitin tantancewa na Accord, Elder Ibe Thankgod, ya tabbatar cewa an tantance Adeleke gabanin zaben fidda gwanin da za a yi a ranar Laraba.



