DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar Accord ta bai wa Adeleke takarar gwamnan Osun

-

Jam’iyyar Accord ta ayyana gwamnan Osun Ademola Adeleke a matsayin dan takara daya tilo a zaben fidda gwanin gwamnan jihar

Kasa da sa’o’i 16 bayan Ademola Adeleke ya koma jam’iyyar Accord, shugabancin jam’iyyar na kasa ya amince da shi ya shiga zaben fidda gwani na gwamnoni.

Google search engine

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa Adeleke ya sauya sheka ne da yammacin Talata tare da mataimakinsa, Kola Adewusi, da wasu manyan jami’ai.

Shugaban kwamitin tantancewa na Accord, Elder Ibe Thankgod, ya tabbatar cewa an tantance Adeleke gabanin zaben fidda gwanin da za a yi a ranar Laraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara