DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

-

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar daga tushe.

Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaranta na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, inda ya ce an dauki matakin ne bayan kammala taron kwamitin gudanarwa na kasa da aka gudanar a ranar 27 ga watan Nuwamba, 2025, bisa tanadin kundin tsarin jam’iyyar.

Google search engine

ADC ta kuma sanar da shirinta na gudanar da tarukan zabe a matakin rumfunan zabe, mazabu da kananan hukumomi daga ranar 20 zuwa 27 ga Janairu, 2026, kafin babban taron kasa da aka shirya gudanarwa a watan Fabrairu, 2026 a Abuja.

Jam’iyyar ta ce wannan shiri na da matukar muhimmanci wajen karfafa hadin kan mambobi da tsari a fadin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara