DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

-

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar daga tushe.

Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaranta na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, inda ya ce an dauki matakin ne bayan kammala taron kwamitin gudanarwa na kasa da aka gudanar a ranar 27 ga watan Nuwamba, 2025, bisa tanadin kundin tsarin jam’iyyar.

Google search engine

ADC ta kuma sanar da shirinta na gudanar da tarukan zabe a matakin rumfunan zabe, mazabu da kananan hukumomi daga ranar 20 zuwa 27 ga Janairu, 2026, kafin babban taron kasa da aka shirya gudanarwa a watan Fabrairu, 2026 a Abuja.

Jam’iyyar ta ce wannan shiri na da matukar muhimmanci wajen karfafa hadin kan mambobi da tsari a fadin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara