DCL Hausa Radio
Kaitsaye

SERAP na barazanar gurfanar da ministan shari’a na Nijeriya kan kin aiwatar da hukuncin kotu game da badakalar N6trn na hukumar NDDC

-

Kungiyar kare hakkin dan-adam da tabbatar da gaskiya (SERAP) ta yi barazanar shigar da kara kan Ministan Shari’a da babban Lauyan Nijeriya, Mista Lateef Fagbemi, SAN, saboda rashin aiwatar da hukuncin kotu kan zargin almundahana na Naira tiriliyan 6 da ake tuhumar Hukumar Ci Gaban Niger Delta (NDDC) da yi.

A cikin wata wasika da aka sanya ranar 13 ga Disamba, kungiyar ta umurci Fagbemi da ya aiwatar da hukuncin da Alh. Justice Gladys Olotu ta bayar a ranar 10 ga Nuwamba, 2025.

Google search engine

Kotun ta umurci Fagbemi da Shugaba Bola Tinubu da su “fitar da sunayen wadanda ake zargi da almundahana a cikin Naira tiriliyan 6 da aka ware don aiwatar da ayyuka 13,777 da aka dakatar da su da kuma gudanar da NDDC tsakanin 2000 da 2019.”

Hukuncin ya kuma umarci wallafa “rahoton binciken kudi na NDDC da aka mika ga gwamnatin tarayya a ranar 2 ga Satumba, 2021.” SERAP ta bayyana cewa rashin aiwatar da hukuncin wulakanci ne ga tsarin shari’a da doka a kasar.

Kungiyar ta gargadi cewa ci-gaba da kin aiwatar da hukuncin na iya sanya Fagbemi da Shugaba Tinubu fuskantar daukar alhakin kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara