DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar dattawan Arewacin Nijeriya ta bukaci a gaggauta janye yarjejeniyar hukumar haraji ta Nijeriya da kasar Faransa

-

Kungiyar dattawan Arewa ta bukaci gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta soke yarjejeniyar fahimta da Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (FIRS) ta kulla da hukumar haraji ta Faransa,, tana mai cewa yarjejeniyar na barazana ga ikon tattalin arziki da tsaron kasa.

A wata budaddiyar wasika da ta aikewa gwamnatin Nijeriya, majalisar dattawa da majalisar wakilai, kungiyar ta bayyana yarjejeniyar a matsayin “hadari ga bayanan haraji,” wadda za ta iya bai wa wata kasa ikon mallakar muhimman bayanan tattalin arzikin Nijeriya.

Google search engine

Wasikar wadda mai magana da yawun kungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere ya sanya wa hannu, ta ce yarjejeniyar ta wuce hadin gwiwar fasaha kawai, tana mai gargadin cewa tana zama wata hanya kai tsaye da ba ta da kariya zuwa cibiyar tsarin haraji na Nijeriya, tare da mika bayanai masu matukar muhimmanci ga ikon wata kasa ta waje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Eng Faruk Ahmad ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban hukumar NMDPRA

Shugaba Tinubu ya bukaci majalisa ta sahale masa nada sabbin shugabannin hukumomin kula da man fetur bayan da Injiniya Farouk Ahmed, ya yi murabus a...

FIFA ta sanya $60 a matsayin kudin tikitin kallon kofin duniya na 2026

Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta ƙaddamar da sabon rukuni na tikiti a dalar Amurka 60 ga kowane ɗayan wasannin 104 na Gasar Kofin...

Mafi Shahara