DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

-

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050, yana mai cewa ta’addanci a Sahel da raunin hadin kan kasa da kasa na kawo cikas ga ci-gaban yankin.

Touray ya bayyana haka ne a taron shugabannin ECOWAS karo na 69 an Abuja, inda ya ce wadannan kalubale na tilasta wa kasashen yankin daukar matakai masu wahala da ka iya shafar dunkulewar kungiyar.

Google search engine

Touray ya kara da cewa duk da matsalolin tsaro da siyasa da ke karkatar da hankali daga ci-gaba, ECOWAS za ta ci gaba da mayar da hankali kan hadewar tattalin arziki domin cimma burin Vision 2050.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara