Hukumar kwallon kafar Nijeriya ta fara dawo da burin zuwa gasar cin kofin duniya ta 2026
Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Najeriya (NFF) ta shigar da ƙorafi kan zargin tawagar DR Congo
da coge a ‘yan wasan da ta yi wasannin share fagen Kofin Duniya na 2026 da su.
NFF ta ce wasu ‘yan wasan da suka sauya ƙasa na riƙe da shaidar ƙasa biyu, abin da kundin tsarin mulkin DR Congo bai yarda da shi ba.
Lamarin da wasu ke tunanin ya iya sake buɗe wa Super Eagles hanyar zuwa gasar da za a yi a Amurka, Kanada da Mexico.


