DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kiris ya rage na ajiye mukamina na minista a lokacin Buhari – Lai Mohammed

-

Tsohon Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ya bayyana cewa ya kusan yin murabus a wani lokaci da ya kira mafi wahala a lokacin mulkin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari.

Ya bayyana haka ne a Abuja yayin ƙaddamar da littafinsa mai taken “Headlines & Soundbites,” inda ya ce kasancewarsa a tsakiyar harkokin gwamnati na tsawon shekaru takwas ya ɗora masa nauyin fayyace gaskiya da gyara fahimtar da aka yi kuskure game da mulkin Buhari.

Google search engine

Mohammed ya ce littafin ya bayyana yadda aka tafiyar da sadarwar gwamnati a lokutan rikici, labaran ƙarya da matsin lamba, yana mai jaddada cewa ‘yan Afirka su ne ya kamata su ba da labarin kansu.

A taron, Ministan Yaɗa Labarai na yanzu, Mohammed Idris, ya yaba da rawar da Lai Mohammed ya taka, yayin da Halima Buhari ta ce mahaifinta yana sane da suka da yabon da ake yi wa gwamnatinsa a lokacin mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara