DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Magoya bayan Buhari za su ci gaba da faɗa wa Gwamnatin Tinubu gaskiya domin tabbatar adalci – Alhassan Ado Doguwa

-

Dan Majalisar Wakilai daga Kano kuma jagoran ’yan Arewa a Majalisar, Alhassan Ado Doguwa, ya ce magoya bayan marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari za su cigaba da “faɗin gaskiya ga masu mulki” domin tabbatar da ɗorewar APC gabanin zaɓen 2027.

Doguwa ya bayyana hakan ne an Abuja yayin ƙaddamar da littafin tsohon Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed, inda ya ce biyayya ga jam’iyya ba ya na nufin shiru idan abubuwa ba su tafiya daidai ba. Ya ce hakan zai taimaka wa jam’iyyar kada ta rasa kusanci da jama’a kafin zaɓe.

Google search engine

Ya jaddada cewa Buhari ya rasu a matsayin cikakken mamba na APC, yana mai cewa wannan muhimmin abin koyi ne ga magoya bayansa, musamman a Arewa. A cewarsa, ’yan Buhari za su cigaba da kare muradun talakawa da marasa ƙarfi kamar yadda tsohon shugaban ya yi.

Doguwa ya ƙara da cewa Arewa za ta ci gaba da kasancewa a dunkule a siyasa, inda malamai da sarakuna za su taka rawa wajen wayar da kan jama’a da ƙarfafa shigarsu cikin harkokin mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara