Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa matsalar diflomasiyya da ta taso tsakanin Nijeriya da Amurka kwanan nan ta shawo kanta bayan tattaunawa mai dorewa tsakanin kasashen biyu.
Ministan yada Labarai, Mohammed Idris, ya bayyana haka a taron manema labarai na karshen shekara a Abuja ranar Litinin inda ya ce rikicin ya samo asali ne bayan maganganun Shugaba Donald Trump da suka yi zargin kisan kiristoci a Nijeriya da yiwuwar shiga da sojoji, amma an warware ta hanyar tattaunawa.
Idris ya ce Nijeriya ta gudanar da al’amuran cikin natsuwa da ka’ida, wanda ya haifar da dangantaka mafi karfi da Amurka. Ya nuna sabuwar yarjejeniya kan hadin gwiwar kiwon lafiya a matsayin hujja ta kyakkyawar alaka.
Wannan yarjejeniya ta shekaru biyar ta kai dala biliyan 5.1, inda Amurka za ta bayar da dala biliyan 2.1 a matsayin tallafi, Nijeriya kuma ta bada dala biliyan 3 don inganta tsarin kiwon lafiya.
Ministan ya ce wannan yarjejeniya za ta inganta samar da lafiya, ceci rayuka, da jawo karin zuba jari a kasar. Ya kuma kara da cewa ci-gaban ya nuna cewa damuwa kan tabarbarewar dangantaka tsakanin Nijeriya da Amurka ba su da tushe.



