DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wadanda suka yi garkuwa da ‘yan Mauludi 28 a jihar Plateau na neman kudin fansa N1.5m kan kowane mutum

-

‘Yan bindiga da ake zargin sace mutane 28 a ƙauyen Zak, karamar hukumar Wase, Bashar, jihar Filato, sun tuntubi iyalan wadanda suka yi garkuwa da su suna neman a biya su kuɗin fansa na Naira miliyan 1.5 ga kowane mutum.

An sace mutanen ne a daren Lahadi yayin da suke kan hanyarsu zuwa bikin Maulidi a ƙauyen Sabon Layi da ke Bashar. An kai musu hari a mota, aka sace su, aka bar motar a wurin.

Google search engine

Ibrahim Musa, ɗaya daga cikin ‘yan uwa, ya shaida wa Daily Trust cewa yan bindigan sun tabbatar musu cewa suna cikin koshin lafiya amma sun dage a biya N1.5m ga kowane mutum. Yace sun roƙi ’yan bindigan su yi tausayi saboda iyalan fursunonin ba su da ƙarfin wadannan kuɗin.

Hukumar ‘yan sanda ta jihar Filato ta tabbatar da lamarin a ranar Litinin, tana mai cewa suna kan binciken al’amarin. Al’ummar yankin sun bukaci ƙarin tsaro don rage satar mutane, fashi da makami, da satar shanu a Karamar Hukumar ta Wase.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara