‘Yan bindiga da ake zargin sace mutane 28 a ƙauyen Zak, karamar hukumar Wase, Bashar, jihar Filato, sun tuntubi iyalan wadanda suka yi garkuwa da su suna neman a biya su kuɗin fansa na Naira miliyan 1.5 ga kowane mutum.
An sace mutanen ne a daren Lahadi yayin da suke kan hanyarsu zuwa bikin Maulidi a ƙauyen Sabon Layi da ke Bashar. An kai musu hari a mota, aka sace su, aka bar motar a wurin.
Ibrahim Musa, ɗaya daga cikin ‘yan uwa, ya shaida wa Daily Trust cewa yan bindigan sun tabbatar musu cewa suna cikin koshin lafiya amma sun dage a biya N1.5m ga kowane mutum. Yace sun roƙi ’yan bindigan su yi tausayi saboda iyalan fursunonin ba su da ƙarfin wadannan kuɗin.
Hukumar ‘yan sanda ta jihar Filato ta tabbatar da lamarin a ranar Litinin, tana mai cewa suna kan binciken al’amarin. Al’ummar yankin sun bukaci ƙarin tsaro don rage satar mutane, fashi da makami, da satar shanu a Karamar Hukumar ta Wase.



