DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jihohin Yobe da Benue ne suka fi samun yawan ‘yan gudun hijira a Nijeriya – NHRC

-

Hukumar Kare Haƙƙin Dan Adam ta Ƙasa (NHRC) ta bayyana cewa Jihohin Yobe da Benue ne ke kan gaba wajen yawan ‘yan gudun hijira a Nijeriya a tsakiyar shekarar 2025.

Rahoton hukumar ya nuna cewa Yobe ta samu ‘yan gudun hijira 2,047, yayin da Benue ke da 1,850, lamarin da ke nuna tsananin matsalar tsaro a Arewa maso Gabas da Arewa ta Tsakiya.

Google search engine

Babban Sakataren NHRC, Dr Tony Ojukwu (SAN), ya bayyana hakan ne yayin gabatar da kundin bayanan hukumar, kamar yadda kafar dillancin labarai ta Nijeriya (NAN) ta ruwaito.

Ojukwu ya ce jimillar ‘yan gudun hijira da aka yi rajista sun kai 9,290 a jihohi 11, sakamakon hare-haren ‘yan bindiga, rikicin manoma da makiyaya, da ta’addanci, wanda ya lalata rayuwar jama’a da hanyoyin samun abinci.

Dr Ojukwu ya ƙara da cewa yara ne suka fi shan wahala, inda suka kai kashi 82 cikin 100 na mutanen da abin ya shafa. Ya kuma ce akwai masu neman mafaka 215 da ke fuskantar matsalar rajista a Taraba da Cross River, tare da ‘yan gudun hijira 583, galibinsu a waɗannan jihohin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara