Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke jinkirta aiwatar da hukuncin Kotun Koli da ya umurci Gwamnatin Tarayya ta raba kudaden FAAC kai tsaye ga kananan hukumomi.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na facebook, Atiku ya ce jinkirin ba kawai rashin kulawa bane, har ma yana nuni da nuna kin bin doka domin siyasa. Ya bayyana cewa gwamnatin Tarayya tana amfani da aiwatar da kundin tsarin mulki a matsayin hanyar tilasta gwamnonin adawa shiga jam’iyyar APC da tabbatar da cewa gwamnonin APC suna ƙarƙashin ikon ta.
Ya kara da cewa, “Hukuncin Kotun Koli ƙarshe ne, ba zaɓi ba. Rashin aiwatarwa kai tsaye karan tsaye ne ga kundin tsarin mulki kuma cin zarafi ne ga alkawarin da Shugaba ya ɗauka ga ’yan Nijeriya.”
Atiku ya jaddada cewa wannan mataki yana jefa kananan hukumomi cikin matsala, yana hana ci-gaban yankuna, da ƙara talauci a matakin ƙasa, inda hanyoyi suka lalace, cibiyoyin lafiya ba sa aiki, kuma albashin ma’aikata bai biya ba.
Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya ya bukaci Shugaba Tinubu da ya umarci Lauyan Gwamnatin Tarayya nan da nan ya aiwatar da hukuncin, yana mai cewa rashin yin hakan na nuna cewa mulkin jam’iyya ya fi adalcin tattalin arziki da bin doka muhimmanci, kuma rayuwar ’yan ƙasa ta fi daukar hankali fiye da bukatun siyasa.



