DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yanke wa daurarru sama da 27,000 hukunci a Nijeriya cikin shekarar 2025

-

Hukumar kula da gidajen ajiya da gyaran hali ta Nijeriya ta bayyana cewa akalla daurarru 27,416 ne aka yanke wa hukunci a fadin kasar cikin shekarar 2025.

 

Google search engine

Ta kuma ce a halin yanzu akwai mutane 50,703 da ke jiran shari’a a daidai lokacin da ake bankwana da 2025.

 

Wannan dai na cikin wani sabon rahoto da hukumar ta fitar, wanda ke nuna irin kalubalen cinkoso da ake samu a gidajen yarin da ke fadin kasar, kamar yadda jaridar Punch ta wallafa.

 

A hannu guda, hukumar ta NCoS ta nuna damuwa da cewa yawan wadanda ke zaman jiran shari’ar na kasancewa wani nauyi ga gwamnati, musamman ta bangaren kudaden da ake kashewa wajen kula da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara