Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya nuna cewa ‘yan Nijeriya masu gudun hijira sama da 26,000 ne aka mayar gida daga kasashe daban daban.
Bayanan rahoton da aka fitar a watan Nuwamban 2025, sun nuna cewa an dawo da su ne daga kasashen Nijar, Chadi da kuma Kamaru da kuma Sudan.
Haka kuma, hukumomi sun tabbatar da cewa a halin yanzu akwai ‘yan Nijeriya fiye da dubu 408 da ke zaune a kasashen waje, a yanayi na gudun hijira.
Hukumomin sun jingina yawaitar samun hakan da samun rikice-rikice daga ayyukan ta’addanci a sassa daban daban na kasar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.



