DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An mayar da ‘yan Nijeriya masu gudun hijira 26,000 gida cikin shekarar 2025 – Rahoto

-

Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya nuna cewa ‘yan Nijeriya masu gudun hijira sama da 26,000 ne aka mayar gida daga kasashe daban daban.

 

Google search engine

Bayanan rahoton da aka fitar a watan Nuwamban 2025, sun nuna cewa an dawo da su ne daga kasashen Nijar, Chadi da kuma Kamaru da kuma Sudan.

 

Haka kuma, hukumomi sun tabbatar da cewa a halin yanzu akwai ‘yan Nijeriya fiye da dubu 408 da ke zaune a kasashen waje, a yanayi na gudun hijira.

 

Hukumomin sun jingina yawaitar samun hakan da samun rikice-rikice daga ayyukan ta’addanci a sassa daban daban na kasar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara