DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun sace mutane da dama a wasu hare hare da suka kai a Katsina

-

Wasu ’yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai hare-hare kan wasu al’ummomi a jihar Katsina, inda suka sace mutane da dama.

Shaidun gani da ido sun shaida wa gidan talabijin na Channels ta wayar tarho a ranar Talata cewa harin ya faru ne a daren Litinin, bayan da ’yan bindigar suka mamaye yankunan, suka kwashe tsawon lokaci suna aikata ta’asa da firgita mazauna wuraren.

Google search engine

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa ’yan bindigar sun fara kai hari a Unguwar Alhaji Barau, daga bisani suka wuce Gidan Dan Mai-gizo da Gidan Hazo, duk a Unguwar Na’alma da ke karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

Duk da haka, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba, yayin da har yanzu ba a tantance adadin mutanen da aka kashe ko waɗanda aka sace ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed, tsohon shugaban hukumar NMMPRA Jaridar Daily Trust ta ce attajirin...

Nijeriya na bin kasashen Nijar, Togo da Benin tulin bashin kudin lantarkin da ya kai N25bn – NERC

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya NERC ta ce, kasar na bin kasashen Togo, Nijar da Benin bashin dala $17.8m — kimanin N25bn na lantarkin...

Mafi Shahara