DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun ceto mutane shida da aka sace a Kaduna

-

Dakarun rundunar Operation Fansar Yamma sun samu nasarar ceto mutane shida da aka sace a wani sumame da suka gudanar a yankunan Kajuru da Kujama na jihar Kaduna.

Mukaddashin Mataimakin Daraktan yada labarai da huldaa da jama’a na rundunar sojin Nijeriya, sashe na 1, Laftanar Kanal Shuaib Umar, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X a ranar Talata.

Google search engine

Ya ce an gudanar da aikin ceton ne a ranar 5 ga Janairu, 2026, a wani bangare na hare haren da aka kai a ƙananan hukumomin Chikun, Kajuru, Kachia, Kagarko, da kuma yankunan kan iyaka da Kauru.

Bayan fafatawar, sojojin sun ci gaba da binciken yankin tare da samun nasarar ceto mutane shida da aka sace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara