Dakarun rundunar Operation Fansar Yamma sun samu nasarar ceto mutane shida da aka sace a wani sumame da suka gudanar a yankunan Kajuru da Kujama na jihar Kaduna.
Mukaddashin Mataimakin Daraktan yada labarai da huldaa da jama’a na rundunar sojin Nijeriya, sashe na 1, Laftanar Kanal Shuaib Umar, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X a ranar Talata.
Ya ce an gudanar da aikin ceton ne a ranar 5 ga Janairu, 2026, a wani bangare na hare haren da aka kai a ƙananan hukumomin Chikun, Kajuru, Kachia, Kagarko, da kuma yankunan kan iyaka da Kauru.
Bayan fafatawar, sojojin sun ci gaba da binciken yankin tare da samun nasarar ceto mutane shida da aka sace.



