DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan yada labarai ya nesanta kansa da wani rubutu mai taken “Malagi 2027”

-

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Nijeriya, Mohammed Idris, ya nesanta kansa daga wani rubutu na siyasa mai taken “Malagi 2027”, wanda ke hasashe kan zaben gwamnan Jihar Neja na 2027. Ma’aikatar ta ce an wallafa rubutun ne ba tare da sanin ministan ko amincewarsa ba, lamarin da ya kai ga dakatar da mataimakin da ya rubuta shi.

A wata sanarwa da Mataimakin Ministan kan Harkokin Watsa Labarai, Rabiu Ibrahim, ya fitar a ranar Laraba, an ce ministan ya bukaci jama’a su yi watsi da rubutun gaba daya. Sanarwar ta jaddada cewa ministan na mayar da hankali ne kacokan kan aikinsa na gwamnati, ba tare da tsoma kansa cikin maganganun siyasa ba.

Google search engine

Sanarwar ta kuma bayyana cewa an fara bincike kan lamarin tare da dakatar da mataimakin da ya rubuta rubutun nan take. Haka kuma, ta jaddada cewa Ministan da Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, na da kyakkyawar alaka ta fahimtar juna, inda ta ce duk wata jita-jita kan siyasar 2027 na iya lalata wannan hadin kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wasu lauyoyi biyu daga Tanzania sun yi kara a gaban kotu suna kalubalantar zaɓen 2025 da aka gudanar a kasar

Wasu lauyoyi biyu a Tanzania, Tito Magoti da Bob Wangwe, sun kai ƙasar Tanzania gaban Kotun Gabashin Afirka kan zaɓen da aka gudanar a ranar...

Za mu karbi Peter Obi hannu biyu a jam’iyyar LP idan bai samu takara a ADC ba – Datti Baba Ahmed

Tsohon ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party LP,Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya bayyana cewa Peter Obi zai samu tarba a LP idan har...

Mafi Shahara