DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun kakaba wa manoma harajin dubu 50 ga kowace gona a jihohin Kano da Katsina kafin su girbe gonarsu

-

’Yan bindiga da ke tsakanin jihohin Kano da Katsina sun kakaba haraji ga manoma har ₦50,000 a kowace eka ga manoma, musamman masu noman rake, kafin su girbe amfanin gonarsu.

Jaridar The Guardian ta bayyana cewa ’yan bindigar sun kafa sansanoni a Dajin Rugu da ke karamar hukumar Faskari a jihar Katsina da kuma Dajin Falgore a karamar hukumar Doguwa a jihar Kano, inda suke karɓar haraji da yi wa manoman barazana.

Google search engine

Rahoton ya nuna cewa manoman da suka ƙi biyan harajin na fuskantar barazana, lalata amfanin gona, da yiwuwar kai musu hari, lamarin da ya tilasta wa da dama barin gonakinsu,kuma yawanci manoman rake ne suka fi fuskantar wannan matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara