DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sandan sun dakile harin ‘yan bindiga a wani kauyen jihar Gombe

-

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta ce ta dakile yunkurin harin ’yan bindiga a kauyen Guda Lamido, da ke garin Kashere a karamar hukumar Akko kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:00 na safiyar Talata, 13 ga Janairu, inda aka samu rahoton cewa wasu ’yan bindiga sun yi yunkurin kutsawa cikin kauyen.

Google search engine

Ya ce jami’an ’yan sanda tare da ’yan banga da mafarauta sun gaggauta kai dauki, inda suka fafata da ’yan bindigar tare da tilasta musu guduwa zuwa daji.

DSP Abdullahi ya ce babu wanda ya rasa ransa ko ya jikkata, kuma an dawo da zaman lafiya a yankin. Ya kara da cewa an tsaurara sintiri da sa ido domin hana sake aukuwar barazana, tare da yin kira ga jama’a da su cigaba da bai wa hukumomin tsaro hadin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai kan duk wani motsi na barazana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara