DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna alfahari da ku duk da rashin nasarar da aka samu a wasan da aka buga da Morocco a AFCON – Gwamnatin Nijeriya

-

Gwamnatin Nijeriya ta yaba wa tawagar Super Eagles bisa rawar da suka taka a gasar AFCON 2025, tana mai cewa ’yan Nijeriya na alfahari da su duk da ficewarsu a wasan kusa da na ƙarshe.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya ce ’yan wasan sun wakilci ƙasa da mutunci, jajircewa da haɗin kai.

Google search engine

Ministan ya ce, duk da sun sha kashi, Super Eagles sun nuna halayen da ke dacewa da tutar ƙasa, inda ya jaddada cewa saka rigar kore da fari na nufin jarumta, haɗin kai da rashin yanke ƙauna. Idris ya ce ƙoƙarinsu ya fi muhimmanci fiye da sakamakon wasa kawai.

Super Eagles sun fice ne bayan Morocco ta doke su da bugun fenariti 4–2, bayan wasan ya tashi babu ci har bayan ƙarin lokaci.

Hakazalika, mainistan ya ƙarfafa musu gwiwa da su ɗaga kai, su koyi darasi, su dawo da ƙarfi, yana mai tabbatar musu da ci-gaba da goyon bayan ’yan Nijeriya a kodayaushe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara