Gwamnatin Nijeriya ta yaba wa tawagar Super Eagles bisa rawar da suka taka a gasar AFCON 2025, tana mai cewa ’yan Nijeriya na alfahari da su duk da ficewarsu a wasan kusa da na ƙarshe.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya ce ’yan wasan sun wakilci ƙasa da mutunci, jajircewa da haɗin kai.
Ministan ya ce, duk da sun sha kashi, Super Eagles sun nuna halayen da ke dacewa da tutar ƙasa, inda ya jaddada cewa saka rigar kore da fari na nufin jarumta, haɗin kai da rashin yanke ƙauna. Idris ya ce ƙoƙarinsu ya fi muhimmanci fiye da sakamakon wasa kawai.
Super Eagles sun fice ne bayan Morocco ta doke su da bugun fenariti 4–2, bayan wasan ya tashi babu ci har bayan ƙarin lokaci.
Hakazalika, mainistan ya ƙarfafa musu gwiwa da su ɗaga kai, su koyi darasi, su dawo da ƙarfi, yana mai tabbatar musu da ci-gaba da goyon bayan ’yan Nijeriya a kodayaushe.



