DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Maciji ya yi ajalin Malami a wata lalatacciyar makaranta da ke Abuja

-

Jagoran al’ummar kauyen Jamigbe a mazabar Gawu da ke yankin Abaji a Abuja, Mai Martaba Alhaji Danladi Aliyu, ya tabbatar da rasa ran wani malami mai suna Usman Mohammed sakamakon saran maciji.

 

Google search engine

Lamarin da ya faru a makarantar firamare ta yankin, ya jefa fargaba a cikin zukatan iyaye, dalibai da malamai baki daya, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

 

Da ya ke jawabi, Alhaji Danladi ya ce mamacin ya gamu da ajalinsa ne, bayan da macijin ya shiga ofishinsa ta cikin wani rami ya kuma buya a karkashin kujera.

 

Bayan saran malamin, rahotanni sun nuna cewa macijin ya yi masa tsartuwa a idanunsa, inda jim kadan da mika shi asibiti likitoci suka tabbatar da rasuwar sa.

 

Alhaji Danladi ya dora alhakin faruwar lamarin da lalacewar makarantar da yayi sanadiyar bai wa halittu kamar maciji damar shiga ciki.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara