Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya isa birnin Ilorin na Jihar Kwara domin jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa harin da aka kai wa al’ummar Woro da ke Karamar Hukumar Kaiama a ranar Talata.
Kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito, jirgin Mataimakin Shugaban ya sauka a Filin Jirgin Sama na Janar Tunde Idiagbon da misalin karfe 10:30 na safiyar Asabar, inda ya zo domin nuna alhini da duba halin tsaro.
Mataimakin Shugaban ya samu rakiyar Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, Sanata Ali Ndume, da Sanata Ovie Omo-Agege zuwa jihar.
A filin jirgin saman, Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, tare da Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kwara, Yakubu Salihu, da Sanatan Kwara Ta Arewa, Sadiq Umar, ne suka tarbe shi.


