Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya kare matakin Majalisar kan gyaran Dokar Zaɓe, yana mai cewa masu sukar aikin na yanke hukunci ne tun kafin kammala bin tsarin dokar.
Akpabio ya jaddada cewa Majalisar ba ta cire tsarin aika sakamakon zaɓe ta na’ura daga dokar ba, sai dai ta ɗora ayar tambaya kan sharadin aika sakamakon a lokacin da ake yin zaɓe.
A cewar wata sanarwa da jaridar Punch ta ruwaito, Akpabio ya yi wannan bayani ne a Abuja yayin da ya halarci bikin kaddamar da littafin The Burden of Legislators in Nigeria na Sanata Effiong Bob, inda ya kasance bako na musamman.


