Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya Sanata Shehu Sani ya bayyana cewa akwai bukatar ‘yan majalisar Amurka su sake yin bincike kan zargin da suke yi wa Kwankwaso da wasu kungiyoyi na tauye ‘yancin addini.
Shehu Sani ya bayyana haka ne a shafinsa na X, yana mai cewa a lokuta da dama, kungiyoyin Miyetti Allah da Miyetti Allah Kautal Hore ba sa tsira daga fuskantar farmakin ‘yan ta’adda.
Kazalika ya ce babu wata hujja da ke nuna cewa Kwankwaso ya musgunawa wani bangare na addini, yana mai cewa zamanin mulkinsa a Kano ya isa shaida.



