Ministan ayyuka na NIjeriya David Umahi ya yi alkawarin sauka daga mukaminsa muddin aikin titin Abuja-Kaduna-Kano bai fito da inganci ba.
Umahi ya bayyana haka ne a lokacin da yake kare kasafin kudin ma’aikatarsa a gaban majalisar dokokin Nijeriya, kamar yadda Channels TV ya wallafa.
An samu tambayoyi kan dalilan da suka sanya ma’aikatar ayyuka ta bai wa wani kamfani da ba a san shi ba aikin, sai dai Umahi ya kare matakin da cewa kamata yayi a mayar da hankali kan ingancin aiki ba wai shaharar kamfani ba.



