Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya bayar da umarnin a biya ma’aikatan gwamnati albashin watan Fabarairun 2026 a ranar 13 ga wata.
Umarnin na kunshe ne cikin wata sanarwa da fadar gwamnatin ta fitar, tare da cewa an dauki matakin duba da karatowar azumin Ramadan.
A cewar ta, hakan zai taimaka wa ma’aikatan wajen samun saukin tafiyar da al’amura yayin gabatar da ibada.



