DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Marocco ta yanke wa magoya bayan Senegal da suka ta da tarzoma a gasar AFCON 2025 hukunci

-

Wata kotu a ƙasar Morocco ta yanke wa magoya bayan Senegal 18,hukunci bisa laifin ta da tarzoma a wasan karshe na cin kofin Nahiyar Afrika na 2025.

An same su da laifin tayar da hankali da lalata wasu kayayyaki bayan sun kutsa cikin filin wasa, suka jefa kujeru, tare da arangama da jami’an tsaro sakamakon bugun fanareti da aka bai wa ƙasar mai masaukin baki.

Google search engine

Duk da cewa Senegal ta doke Morocco da ci 1–0, tarzomar ta jawo asarar fiye da dala $476,000, kuma an dakatar da wasan na ɗan lokaci.

Kotun ta yanke wa mutum 11 hukuncin ɗaurin shekara guda, mutane huɗu watanni shida, sai wasu huɗu watanni uku.

Lauyoyin masu laifin sun ce hukuncin ya yi tsauri, kuma sun bayyana aniyar ɗaukaka ƙara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya yi kira da a zauna lafiya gabanin zaɓen Abuja, Kano da Rivers

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a, jami’an tsaro da jami’an Hukumar zaɓe Mai zaman kanta (INEC) da su gudanar...

Gwamnatin Nijeriya za ta kafa kwalejin koyon likitanci ta sojoji don magance karancin likitoci

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da shirin kafa kwalejin koyon likitanci ta soji "Armed Forces College of Medicine and Health Sciences" a matsayin wani mataki na...

Mafi Shahara