Akalla mutum 30 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka bace bayan harin ’yan bindiga a kauyen Dutsin Dan Ajiya da ke karamar hukumar Anka a jihar Zamfara.
Rahotanni sun ce maharan sun kai farmakin ne da tsakar dare na ranar Alhamis zuwa safiyar Juma’a, inda suka rufe hanyoyin shiga kauyen tare da bude wuta kan mai uwa da wabi.
Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa bayan harin ne aka gano gawarwakin mutum 30, yayin da wasu suka jikkata, wasu kuma har yanzu ba a san inda suke ba.
Lamarin ya faru ne kasa da awanni 48 bayan gwamnatin jihar Zamfara ta kaddamar da sabbin kayan yaki da jiragen sa ido marasa matuki domin karfafa yaki da matsalar tsaro.
Kodayake Gwamnan ya umurci mataimakinsa, Mani Mumuni, da ya kai ziyara yankin domin jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, rundunar ’yan sanda ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba.



