DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƴan adaidaita ne suka yi jigilar kayan zaben kananan hukumomin Abuja

-

An tura babura masu kafa uku da aka fi sani da Keke NAPEP domin jigilar muhimman kayayyakin zabe na INEC zuwa rumfunan zabe a zaben kananan hukumomin Babban Birnin Tarayya (FCT).

An ga kekunan na tsaye a wasu cibiyoyin rarraba kaya, inda jami’an zabe ke tabbatar da an kulle akwatunan zabe da takardun sakamako yadda ya kamata kafin a tura su zuwa unguwanni daban-daban a fadin Abuja.

Google search engine

Jaridar The Nation ta ruwaito amfani da Keke NAPEP na zama hanya mai sauki kuma mai rahusa wajen kai kayan zabe zuwa matakin karshe, musamman a wuraren da manyan motoci ke fuskantar cunkoso ko matsalar shiga.

Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu rahotannin koke-koke masu yawa dangane da rarraba kayan zaben a FCT, duk da cewa masu sa ido na ci gaba da bibiyar yadda ake gudanar da aikin domin kauce wa jinkiri ko wata tangarda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan 99 domin rigakafin cutar mahaukacin kare

Gwamnatin jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan 99 domin fara shirin rigakafin cutar mahaukacin kare (rabies), inda ake sa ran yi wa akalla...

Wike ya koka kan ƙarancin masu fitowa zabe a Abuja

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda ake gudanar da zaɓen kananan hukumomi cikin lumana a fadin Abuja, duk da...

Mafi Shahara