Rahotanni daga Arise News sun nuna cewa manyan jam’iyyun adawa guda uku, NNPP, PDP, da ADC ba su bayyana a takardun zaɓe na zaben cike gurbin kujeru biyu a majalisar dokokin jihar Kano da ake gudanarwa a ranar Asabar ba.
Zaɓen na cike gurbi ne na kujerun da suka samu rashin cancanta bayan rasuwar tsoffin ‘yan majalisa a bara, wadanda suka kasance membobin NNPP kafin rasuwarsu.
Rahoton ya kara da cewa jam’iyyun siyasa tara ne aka jera a takardun zaɓen, ba tare da PDP, NNPP da ADC ba.



