Kotun tarayya da ke Abuja ta amince da buƙatar Gwamnati na gurfanar da mutane biyar da ake zargi da alaƙa da fitaccen dan bindiga Bello Turji, bayan sun ƙi bayyana a gaban kotu sau uku a jere duk da sammacin da aka kai.
Mai shari’a Emeka Nwite ne ya yanke hukunci bayan lauyan gwamnatin tarayya, ya nemi a aiwatar da tanadin Sashe na 352(4) na dokar gudanar da Shari’ar laifuka (ACJA) ta 2015, ganin cewa ba a samu waɗanda ake tuhuma ba duk da umarnin kama su.
Kotun ta bayyana cewa duk da fitar da sammacin kama mutanen, jami’an tsaro sun kasa gano inda suke domin gurfanar da su, sakamakon haka, alƙalin ya amince da a ci gaba da shari’ar ba tare da halartar su ba, tare da ɗaga sauraron shari’ar zuwa ranar 13 ga Afrilu domin ci gaba da gabatar da shaidu.



