DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta amince da a gurfanar da mutanen da ake zargi da alaka da Bello Turji 

-

Kotun tarayya da ke Abuja ta amince da buƙatar Gwamnati na gurfanar da mutane biyar da ake zargi da alaƙa da fitaccen dan bindiga Bello Turji, bayan sun ƙi bayyana a gaban kotu sau uku a jere duk da sammacin da aka kai.

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya yanke hukunci bayan lauyan gwamnatin tarayya, ya nemi a aiwatar da tanadin Sashe na 352(4) na dokar gudanar da Shari’ar laifuka (ACJA) ta 2015, ganin cewa ba a samu waɗanda ake tuhuma ba duk da umarnin kama su.

Google search engine

Kotun ta bayyana cewa duk da fitar da sammacin kama mutanen, jami’an tsaro sun kasa gano inda suke domin gurfanar da su, sakamakon haka, alƙalin ya amince da a ci gaba da shari’ar ba tare da halartar su ba, tare da ɗaga sauraron shari’ar zuwa ranar 13 ga Afrilu domin ci gaba da gabatar da shaidu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara