DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ofishin jakadancin Amurka ya soke neman biza a Abuja saboda fargabar zanga-zanga

-

Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya ya soke dukkan alƙawuran neman biza na ranar 4 ga Maris, 2026 a Abuja, sakamakon yiwuwar zanga-zanga da ka iya barkewa saboda rikicin Amurka da Iran.

Sanarwar da ofishin ya fitar ta ce akwai barazanar zanga-zanga a Babban Birnin Tarayya, don haka ta bukaci ’yan ƙasar Amurka da ke Abuja su zauna a gidajensu tare da kauce wa wuraren taro. Ta kuma ce za a tuntubi masu neman biza domin sake tsara musu sabuwar rana.

Google search engine

Matakin na zuwa ne bayan rahotannin mutuwar jagoran addinin Iran, Ali Khamenei, lamarin da ya kara tsananta rikicin da ke gudana a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ofishin ya jaddada cewa sashen jakadanci na Abuja da ofishin jakadanci a Legas za su ci gaba da aiki, tare da shawartar jama’a su rika bibiyar shafinsu domin samun karin bayani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara