DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba ni da wani dan takara shafaffe da mai a 2027 bayan Tinubu – Uba Sani

-

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ba shi da dan takarar da ya fi so gabanin zabukan fidda gwani na 2027, yana mai cewa ba zai tsoma baki a tsarin zaben ’yan takara ba.

Uba Sani ya bayyana haka ne yayin buda baki da ’yan Majalisar Dokokin jihar, inda ya bukaci masu neman mukamai su nemi goyon bayan mambobin jam’iyya maimakon dogaro da uban gida. Ya ce zai mara wa duk wanda ya samu rinjaye a zabukan fidda gwani na APC.

Google search engine

Sai dai ya ce dan takarar da yake goyon baya shi ne Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, a zaben 2027.

Gwamnan ya kuma yi kira ga mambobin jam’iyya su hada kai, yana mai cewa tsaro a Kaduna ya inganta tun bayan hawansa mulki a 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara