DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai yiyuwar mutum 2 sun rasa rayukansu a rikicin kabilanci a jihar Adamawa

-

Rahotanni daga jihar Adamawa na cewa mutum biyu sun rasa rayukansu a sabon rikicin da ya tashi tsakanin al’ummomin Chobo da Bachaman a karamar hukumar Lamurde, ta jihar.

Mai magana da yawun ‘yan sanda na jihar, Suleiman Yahaya-Nguroje, ya ce rikicin ya barke ne a daren Asabar bayan wasu matasan Chobo sun farmaki garin Lamurde, inda suka yi harbi, abin da ya sa matasan Bachaman suka yi ramuwar gayya.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito an tura jami’an ‘yan sanda domin dawo da zaman lafiya, yayin da ake ci gaba da tattara rahotannin hasarar rayuka.

Wannan rikici wanda ya samo asali ne a kan rikicin kasa a yankin, wanda a cikin watanni shida da suka gabata ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 30, musamman mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara