Rahotanni daga jihar Adamawa na cewa mutum biyu sun rasa rayukansu a sabon rikicin da ya tashi tsakanin al’ummomin Chobo da Bachaman a karamar hukumar Lamurde, ta jihar.
Mai magana da yawun ‘yan sanda na jihar, Suleiman Yahaya-Nguroje, ya ce rikicin ya barke ne a daren Asabar bayan wasu matasan Chobo sun farmaki garin Lamurde, inda suka yi harbi, abin da ya sa matasan Bachaman suka yi ramuwar gayya.
Jaridar Punch ta ruwaito an tura jami’an ‘yan sanda domin dawo da zaman lafiya, yayin da ake ci gaba da tattara rahotannin hasarar rayuka.
Wannan rikici wanda ya samo asali ne a kan rikicin kasa a yankin, wanda a cikin watanni shida da suka gabata ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 30, musamman mata.



