Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi ya yi rajista a ADC a ranar Asabar, inda ya jaddada cewa zaɓen 2027 zai kasance tsakanin ‘yan Najeriya da shugabanci mara inganci.
Obi ya ce yankin Kudu maso Gabas na da hakkin samun shugaban kasa, yana mai cewa babu wani yanki da ya fi shi a Najeriya.
Ya kuma jaddada bukatar fitar da ‘yan Najeriya daga talauci don rage rashin tsaro, tare da karfafa masu rajista su yi kokarin jawo sabbin mambobi zuwa ADC.
A wannan rana, Senator Victor Umeh da tsohon dan majalisa Ben Obi ma sun kammala rajista a jam’iyyar a kananan hukumomin Agulu da Awka, Anaocha da Awka South.



