DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar lafiya ta duniya ta koka kan irin kudaden da ake kashewa a yake-yake duk da yunwar da ake fama da ita a fadin duniya

-

Babban Daraktan Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya soki yadda kasashen duniya ke kashe makudan kudade wajen yaki, yana mai cewa hakan na nuna cewa an karkatar da muhimmancin abubuwan da ya kamata a ba fifiko a kai.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, ya ce kudaden da ake kashewa kan harkokin soja a duniya sun kai dala tiriliyan 2.7 a cikin shekara guda, alhali kiyasin MDD ya nuna cewa dala biliyan 93 kacal ake bukata a duk shekara domin kawo karshen yunwa a duniya nan da shekarar 2030.

Google search engine

Ya ce hakan na nufin kasashen duniya na kashe kusan sau 30 fiye da haka wajen yaki da juna maimakon tabbatar da cewa kowa ya samu abinci, yana mai cewa wannan bambanci na nuna gazawar duniya wajen tinkarar matsalar yunwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara