Wani yaro mai shekaru 16 mai suna Emmanuel Danladi ya harbe abokinsa Titus Joseph mai shekara 15 har lahira da bindigar mahaifinsa a garin Kwamba da ke Suleja a Jihar Niger.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da yaran biyu ke wasa a gidan Emmanuel, inda ya dauki bindigar da mahaifinsa Danladi Baba ke amfani da ita a kungiyar sa-kai, ya harbi abokin nasa a ciki, wanda daga bisani ya mutu.
Mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar, Wasiu Abiodun, ya ce an kama Emmanuel da mahaifinsa, sannan aka kai gawar mamacin babban asibitin Suleja yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.



