DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani yaro dan shekaru 16 ya halbe abokinsa da bindiga yayin da suke wasa a jihar Niger

-

Wani yaro mai shekaru 16 mai suna Emmanuel Danladi ya harbe abokinsa Titus Joseph mai shekara 15 har lahira da bindigar mahaifinsa a garin Kwamba da ke Suleja a Jihar Niger.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da yaran biyu ke wasa a gidan Emmanuel, inda ya dauki bindigar da mahaifinsa Danladi Baba ke amfani da ita a kungiyar sa-kai, ya harbi abokin nasa a ciki, wanda daga bisani ya mutu.

Google search engine

Mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar, Wasiu Abiodun, ya ce an kama Emmanuel da mahaifinsa, sannan aka kai gawar mamacin babban asibitin Suleja yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Ban shirya yin yarjejeniyar sulhu da Iran don kawo karshen yakin da ake yi ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu bai shirya yin wata yarjejeniya da Iran domin kawo karshen rikicin da ke kara tsananta tsakanin kasashen...

Mafi Shahara