DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hadin kai tsakanin hukumonin tsaro tare da masu ruwa da tsaki nada matukar muhimmanci wajen tabbatar da tsaro-Christoper Musa

-

Hadin kai tsakanin hukumonin tsaro tare da masu ruwa da tsaki nada matukar muhimmanci wajen tabbatar da tsaro-Christoper Musa

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya (CDS), Janar Christopher Musa, ya ce rundunar soji na ci gaba da wayar da kan sojoji kan hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro domin kare makarantu daga hare-hare.

Google search engine

Ya bayyana haka ne a yayin bude taron kwana biyu kan makarantun tsaro a hedikwatar runduna ta daya ta sojojin Nijeriya dake Kaduna, CDS ya jaddada muhimmancin samar da muhimman abubuwa kamar babura da na’urorin sadarwa domin isa makarantu cikin hanzari a lokacin da ake bukata.

Wanda ya samu wakilcin Manjo Janar Emeka Onumajuru, ya ce, “Rundunar Sojin Nijeriya ta ‘yan Nijeriya ce kuma za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen ganin an kare al’umma, tare da yin aiki da dukkanin hukumomin tsaro.

Babban kwamandan rundunar soji ta daya (GOC), Manjo Janar Mayirenso Saraso, ya kuma yi kira da a hada kai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaro a makarantun jihar.

Kwamishinan tsaro na harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya ce tsakanin watan Yulin 2021 zuwa Maris 2024, jihar Kaduna ta fuskanci sace yara ‘yan makaranta da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara