DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yan yankin Neja Delta basu da dalilin yin zanga-zanga ga Tinubu inji ministan harkokin yankin

-

 

Google search engine

Ministan harkokin Neja Delta Injiniya Abubakar Momoh yace, al’ummar yankin Kudu maso Kudu ba su da dalilin yin zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu.

Mininstan ya fadi haka ne yayin da yake jawabi ga manema labarai a fadar gwamnati a yau ranar Laraba, Ministan ya ce hakan ya faru ne saboda shugaban kasar ya gudanar da ayyuka da dama da nufin bunkasa yankin ba kawai ba, har ma da karfafa matasa.

Ya kara da cewa, a yankin na Neja Delta, Shugaban kasa ya yi abubuwa da yawa kuma ba ya tunanin duk wani dan yankin Neja Delta zai ga ya dace ya fito ya ce yana zanga-zangar adawa da rashin shugabanci.

Daga karshe yayi kira ga matasan da su ci moriyar ayyukan da gwamnati tay, kada su lalata komai don su ne manyan gobe kuma su zasu ci moriyar su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara