DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sabbin hare-hare a kananan hukumomi hudu na jihar Benue sun yi ajalin mutum 23

-

Rahotanni na nuni da cewa kalla mutane 23 sun halaka a wasu jerin hare-haren da aka kai a wasu kananan hukumomi hudu na jihar Benue.

Daily Trust ta ruwaito cewa kananan hukumomin da abin ya faru sun hada Guma, Logo, Ukum, da Kwande.

Mazauna yankin sun ce sabbin hare-haren da aka kai a baya-bayan nan sun tilasta wa da dama barin yankunansu.

Shaidun gani da ido sun ce an halaka mutane tara a karamar hukumar Logo, takwas a Ukum, yayin da kananan hukumomin Guma da Kwande aka halaka mutum uku, adadin da ya kai 23 da suka mutu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

APC za ta dare gida biyu; su Ganduje ma duk za su koma PDP – Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana cewa akwai yiyuwar jam’iyyar APC mai mulki za ta rabu nan ba da jimawa ba, tare da...

Matakan da Shugaba Tinubu ke dauka sun taimaka wajen rage talauci a Arewacin Nijeriya – Gwamna Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya bayyana cewa babu wata gwamnati a tarihin Nijeriya da ta zuba jari a harkar noma kamar yadda gwamnatin...

Mafi Shahara