DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun yi ajalin shugaban jam’iyyar APC a jihar Ondo bayan sun karbi kudin fansa Naira milyan 5

-

Rahotanni sun tabbatar da cewa masu garkuwa sun kashe shugaban jam’iyyar APC na mazabar 5, Ifon, a karamar hukumar Ose ta jihar Ondo, Nelson Adepoyigi, bayan sace shi a gidansa da ke Ifon kwanan nan.

Masu garkuwar sun fara Neman kudin fansa Naira milyan 100, amma daga bisani bayan tattaunawa suka rage kudin zuwa Naira milyan 5 tare da kayan abinci.

Haka kuma, sun kama wasu mutane biyu da suka kai kudin fansar, inda suka nemi sabon kudin fansa Naira milyan 30 domin sakin mutum ukun da ke hannunsu, ciki har da Adepoyigi da waɗanda suka kai kudin fansar.

Shugaban karamar hukumar Ose, Barr Clement Kolapo Ojo, ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Oluwaseun Ogunniyi, ya fitar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutum 3 tare da sace 26 a Zamfara

Akalla mutane uku ne rayukansu suka salwanta aka kuma sace wasu 26 a wani sabon harin da ‘yan bindiga suka kai karamar hukumar Kauran Namoda...

Hadakar da nake sha’awa ita ce yaki da yunwa da Talauci a fadin Nijeriya

A yayin da ake ci gaba da rade-radin yiwuwar hadaka tsakanin jiga-jigan ‘yan adawa don tunkarar shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027, tsohon dan...

Mafi Shahara