DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun yi ajalin shugaban jam’iyyar APC a jihar Ondo bayan sun karbi kudin fansa Naira milyan 5

-

Rahotanni sun tabbatar da cewa masu garkuwa sun kashe shugaban jam’iyyar APC na mazabar 5, Ifon, a karamar hukumar Ose ta jihar Ondo, Nelson Adepoyigi, bayan sace shi a gidansa da ke Ifon kwanan nan.

Masu garkuwar sun fara Neman kudin fansa Naira milyan 100, amma daga bisani bayan tattaunawa suka rage kudin zuwa Naira milyan 5 tare da kayan abinci.

Google search engine

Haka kuma, sun kama wasu mutane biyu da suka kai kudin fansar, inda suka nemi sabon kudin fansa Naira milyan 30 domin sakin mutum ukun da ke hannunsu, ciki har da Adepoyigi da waɗanda suka kai kudin fansar.

Shugaban karamar hukumar Ose, Barr Clement Kolapo Ojo, ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Oluwaseun Ogunniyi, ya fitar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara