DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zaliha ta ba dan kishiyarta guba a Kaduna

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta kama wata matar aure mai suna Zaliha Shuaibu bisa zargin kashe jaririn kishiyarta dan watanni uku ta hanyar ba shi guba a kauyen Malari da ke karamar hukumar Soba ta jihar.

Wannan lamari ya faru ne a ranar 13 ga Mayu, 2025, a cikin gidan da suke zaune tare da mahaifiyar jaririn, Maryam Ibrahim.

Google search engine

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mansir Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar kamar yadda jaridar PUNCH ta rawaito, inda ya ce an kama wadda ake zargin ne bayan binciken gaggawa da jami’an ‘yan sanda na Sashen Soba suka gudanar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara