Hukumar zaben Nijeriya INEC ta bayyana cewa za ta gudanar da zabukan cike gurbi a mazabun da abin ya shafa a ranar Asabar 16 ga watan Agusta, 2025 a fadin Nijeriya.
Ana dai shirya zabukan ne domin cike guraban kujeru na majalisun tarayya da na jihohi, wadanda aka samu matsala, ko aka samu rauswa, ko soke zaben a kotu.
Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka yayin taron tuntubar juna da jam’iyyun siyasa a Abuja ranar Alhamis.