DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisar dokokin Nijeriya biyu sun bar Labour Party zuwa APC

-

Jam’iyyar Labour Party ta sake rasa wasu ‘yan majalisa guda biyu da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, a daidai lokacin da sauye-sauyen siyasa ke kara kamari gabanin babban zaben 2027.

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio a ranar Alhamis ya sanar da sauya shekar Sanata Neda Imasuen, mai wakiltar Edo ta Kudu, yayin zaman majalisar a Abuja.

Google search engine

A cikin wasikar da ya aike wa majalisar dattawa, Imasuen ya ce matakin nasa ya biyo bayan tattaunawa da al’ummarsa da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da kuma magoya bayansa.

Shima dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Enugu ta Arewa/Kudu Chimaobi Atu, ya fice daga jam’iyyar Labour zuwa APC.

Kakakin majalisar Tajudeen Abbas ne ya sanar da sauya shekar sa a zaman majalisar na ranar Alhamis.

Atu, ya alakanta ficewarsa da rikicin cikin gida na jam’iyyar Labour, wanda ya ce ya yi illa ga ayyukansa na majalisa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara