DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yadda ake ajalin sojoji a fagen daga alamu ne na gazawar gwamnati – Dattawan Arewacin Nijeriya

-

Kungiyar dattawan Arewa ta bayyana yadda ‘yan bindiga suka kashe sojoji kusan 20 a matsayin fito-na-fito da gwamnatin Nijeriya, kuma alama ce ta tabarbarewar tsaro a Arewacin kasar.

Mai magana da yawun kungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere ya bayyana cewa kungiyar ta yi tir da harin da aka kai ma sojojin kuma hakan na nuna irin yadda rashin tsaro ya dabaibaye yankin.

Google search engine

Kungiyar ta gargadi gwamnati kan rashin daukar mataki ya fara sa ‘yan kasa sanya alamun tambaya ga gwamnati game da iya kare rayukansu.

‘Yan bindigar dai sun yi ma sojojin kwantar-bauna a Mariga a cikin farkon wannan satin inda sojoji 20 suka rasa rayukansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Kaso 95 cikin 100 na jihar Kaduna ‘yan APC ne – Uba Sani

Jam’iyyar APC a jihar Kaduna ta karɓi sabbin mambobi, ciki har da ’yan majalisar wakilai guda biyar da kuma ’yan majalisar dokokin jihar Kaduna huɗu...

Mafi Shahara