DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda na neman mijin da ya yi ajalin matarsa a Yobe

-

Rundunar ‘yan sandan Jihar Yobe ta tabbatar da cewa wani Hamisu Ali mai kimanin shekaru 55 ya yi ajalin matarsa mai shekaru 40 a garin Babangida da ke a karamar hukumar Tarmuwa ta Jihar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan jihar, Dungus Abdulkarim ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa, inda ya ce lamarin ya faru ne a ranar safiyar Juma’a.

Google search engine

Ya kuma kara da cewa, a ranar 28 ga Yuni ne suka amsa kira daga mazauna kauyen Koriyel inda suka shaida musu cewa Hamidu ya sassari matarshi inda ya yi sanadiyar ajalinta kuma ya gudu. Amma Rundunar na bakin kokari wajen ganin ya shiga hannu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Hukumar FRSC ta bayyana dalilan yawan afkuwar hadura a titunan Nijeriya

Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta Nijeriya FRSC ta bayyana cewa a mafiya yawan lokuta rashin hakuri, gudun wuce sa'a tare da karya dokokin hanya ne...

Mafi Shahara